Saturday, June 10, 2023
HomeUncategorizedDuba SuMaguzuwa 314 sun karbi musulunci yau a Kano

Maguzuwa 314 sun karbi musulunci yau a Kano

Daga Muryoyi

Akalla maguzawa 314 ne suka karbi addinin musulunci a garin Gidan Goje dake karamar hukumar Takai a yau Litinin,

Maguzawan sun shaidawa majiyar Muryoyi cewa; Ra’ayin kan su ne suka musulunta ba don an tilasta su ba ko kuma don ko wai za’a basu wani abu ba.

Muryoyi ta ruwaito maguzawan sun musulunta ne a hannun shugaban kungiyar Izala na kasa Abdullahi Bala Lau, da Gwamnan jihar Kano, Gwamna Abdullahi Umar Ganduje da shugaban darikar Kadiriyya Sheikh Kariballah Nasiru Kabara, da Sauran manyan malamai daga kungiyoyi daban-daban,

- Advertisement -

Ganduje wanda ke jawabi a madadin gidauniyarsa ta Ganduje Foundation yayi alkawarin za su gina masu babban masallacin Juma’a da makaranta domin ilimantarwa da kara dabbaka addinin Musulunci a Garin na Goje.

Daga bisani an rabawa sabbin musuluntar tufafi, kayan sawa da sauran abubuwan bukata.

LABARAI MASU ALAKA

Leave a Reply

- Advertisment -

MAFI SHAHARA

RA'AYOYIN JAMA'A

%d bloggers like this: