An kashe wadanda suka kai harin Bama-bamai a Maiduguri lokacin ziyarar shugaban kasa –inji IGP
Daga Muryoyi
Shugaban yan sandan Najeriya IGP Alkali Usman Baba ya ce an samu nasarar kashe mafiy yawa daga cikin gungun yan ta’adda da suka harba rokoki ko Bama-bamai a Maiduguri ranar Alhamis daidai lokacinda shugaban kasa Muhammadu Buhari ke kai ziyara a jihar
Muryoyi ta ruwaito IGP Usman ya bayyana haka ne a tattaunawarsa da manema labarai jim kadan da suka kammala wata ganawa da shugaba Muhammadu Buhari a fadarsa ranar Juma’a.
Ya ce yan ta’addan sun harba rokoki a ziyarar shugaban kasar amma cikin taimakon Allah basu samu nasarar cimmma abunda suka so cimmawa ba saboda tsaron da matakan tsaro da aka sanya a jihar ta Borno a lokacin ziyarar shugaban kasar
- Advertisement -
Ya kuma ce shugaban kasa ya basu oda kada su dagawa kowane dan ta’adda kafa