Thursday, March 23, 2023
HomeUncategorizedDuba SuGwamnatin Bauchi Za Ta Rabawa 'Yan Kasuwa Bashin Miliyan 500 don Farfado...

Gwamnatin Bauchi Za Ta Rabawa ‘Yan Kasuwa Bashin Miliyan 500 don Farfado Da Kananan Masana’antu

Daga Abbakar Aleeyu Anache,

Gwamnatin Jihar Bauchi ta ce za ta raba bashin Naira miliyan 500 ga ƴan kasuwa da masu ƙananan sana’o’i domin bunƙasa ƙanana da matsakaitan sana’o’i, SMEs a jihar.

Khalid Ningi, Kataimaki na Musamman ga Gwamna Bala Mohammed kan Harkokin Tallafi ne ya baiyana hakan a tattaunawar da ya yi da Kamfanin Daillancin Labarai, NAN a yau Juma’a a Bauchi.

Sai dai kuma Ningi bai yi ƙarin bayani a kan yawan sana’o’in da za su amfana da bashin ba.

- Advertisement -

Amma kuma ya ce tuni a ka saki kuɗaɗen ta wasu ba kuna domin a hanzarta aiwatar da shirin.

Ya ƙara da cewa gwamnatin ta yi duba ga jinsi, inda za ta samar da daidaito na jinsi a wajen raba bashin domin a samu wakilcin kowanne ɓangaren domin samun cikakkiyar nasarar tsari .

Ya kuma ƙara da cewa gwamnatin jihar da haɗin gwiwa da Gidauniyar Ɗangote sun naira miliyan 200 ga mata masu ƙananan sana’o’i a jihar, inda ya ce kowacce mace da ta amfana da tallafin ta samu Naira dubu 10.

LABARAI MASU ALAKA

Leave a Reply

- Advertisment -

MAFI SHAHARA

RA'AYOYIN JAMA'A

%d bloggers like this: