Daga Muryoyi
Kungiyar majalisar dokoki na jihohin Nigeria 36 sun zabi Gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello a matsyin dan takararsu a zaben shugaban kasa na 2023 a karkashin inuwar jam’iyyar APC.
Bayanin hakan ya fito ne a jawabin bayan taro da kungiyar ta gudanar a Abuja.
Yan majalisar su 365 sun tabbatar da cewa Gwamnan ya ciri tuta kuma ya cancanta a duka matakan shugabancin Nigeria irin wanda kasar nan ke bukata
- Advertisement -
Zuwa yanzu dai ana iya cewa takarar Gwamna Yahaya Bello na ta kara samun tagomashi tun bayan da ya bayyana aniyarsa ta fitowa takara a 2023, mata da matasa da kungiyoyi a Kudu da Arewacin kasarnan ke fitowa suna mara masa baya a kusan kowace rana.