Gwamnatin tarayya ta ce kamfanin NNPC ya samu isasshen man fetur
Daga Muryoyi
Gwamnatin tarayya ta ce kamfanin mai na NNPC ya samu isasshe kuma wadataccen man fetur da zai rarrabawa gidajen mai a faɗin Kasarnan.
NNPC ya buƙaci yan Najeriya sun kwantar da hankalinsu akwai isasshen man fetur kuma kamfanin na aiki da abokan hulɗarsa don tabbatar da cewa ya isa a kowane ɓangare na ƙasar.
Kamfanin ya kuma yi kira ga ƴan Najeriya su ci gaba da haƙuri yayin da ake ƙoƙarin ganin abubuwa sun koma daidai.
- Advertisement -
An shafe kusan mako biyu ana wahalar man fetur a sassan Najeriya wanda hakan ya jawo kunci da damuwa.