Thursday, March 23, 2023
HomeUncategorizedDuba SuAzabar Allah na jiran waɗanda suka kai hari suka kashe mutane a...

Azabar Allah na jiran waɗanda suka kai hari suka kashe mutane a cocin Ondo –inji Buhari

Azabar Allah na jiran waɗanda suka kai hari suka kashe mutane a cocin Ondo –inji Buhari

 

Daga Muryoyi

 

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana kaduwa da bakin ciki game da kisan gillar da akayiwa wasu masu ibada a coci da sanyin safiyar yau inda yan bindiga suka afka masu suka kashe mutane da dama suka jikkata wasu sannan sukayi awon gaba da wasu da har yanzu ba a tantance adadinsu ba.

 

Muryoyi ta ruwaito Shugaba Buhari na cewa baƙin ciki na har abada yana jiran waɗanda suka kai wannan hari duniya da lahira, kuma zasu gamu da azabar Allah tana jiransu a lahira.

 

- Advertisement -

Shugaban kasar ya mika ta’aziyyarsa ga al’ummar Ondo da yan’uwa da abokan wadanda harin ya shafa, sannan ya bukaci duka hukumomin bayar da agajin gaggawa su hanzarta kai daukin gaggawa ga wadanda abun ya shafa

 

Lamarin ya faru ne da safiyar yau Lahadi a cocin  St Francis Catholic Church, dake Owa-luwa Street, a masarautar Owo Kingdom, dake jihar Ondo inda rahotanni farko ke cewa gomman masu ibada sun mutu

LABARAI MASU ALAKA

Leave a Reply

- Advertisment -

MAFI SHAHARA

RA'AYOYIN JAMA'A

%d bloggers like this: