DA DUMI-DUMI: Dagaske yan bindiga sun saki fasinjojin jirgin kasa 11 –inji Tukur Mamu
Daga Muryoyi
Bayan tattaunawa mai tsawo tsakaninsu wakilan Gwamnatin tarayya da yan ta’adda a karshe dai masu garkuwar sun sako fasinjojin jirgin kasa 11 daga cikin wadanda sukayi garkuwa dasu fiye da wata biyu.
Daya daga cikin mai shiga tsakani Babban dan Jarida Malam Tukur Mamu wanda shine mai magana da yawun Dr Ahmed Gumi ya bayyana cewa yan bindigar sun sako mqta 6 maza 5 a yau Asabar.
- Advertisement -
Muryoyi ta ruwaito daga majiyoyi da dama ciki har da Daily Trust cewa yanzu haka a bisa umurnin shugaba Muhammadu Buhari an kwashi duka mutum 11 da suka shaki iskar yancin zuwa Abuja domin duba lafiyarsu kafin a hadasu da iyalansu.