Thursday, March 23, 2023
HomeUncategorizedDuba SuHar gobe talakawa na kaunar APC, zamu ci zabe a 2023 kamar...

Har gobe talakawa na kaunar APC, zamu ci zabe a 2023 kamar yadda mukayi a 2015 da 2019 – inji Buhari

Har gobe talakawa na kaunar APC, zamu ci zabe a 2023 kamar yadda mukayi a 2015 da 2019 – inji Buhari

 

Daga Muryoyi

 

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce ko shakka baya yi jam’iyyar APC ce za tayi nasara a zaben shugaban kasa a 2023 kamar yadda tayi a 2015 da 2019.

 

Shugaban ya bayyana haka ne a lokacinda ya yi wata ganawa da wasu jiga-jigan jam’iyyar domin lalubo dan takarar da yafi cancanta APC ta tsaida a babban zabe mai zuwa wanda taron ya gudana a daren jiya Lahadi a Abuja.

 

- Advertisement -

Muryoyi ta ruwaito Buhari na cewa zuwa yanzu ya tuntubi kungiyar Gwamnonin APC, da su kansu yan takarar da sauran masu ruwa da tsaki a jam’iyyar kuma ganawar tana haifar da d’a mai ido.

 

 

Shugaba Buhari yayi amanna har gobe talakawa suna kaunar jam’iyyar APC kuma ita zata yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben shugaban kasa da na Majalisun tarayya da Gwamnoni a 2023

LABARAI MASU ALAKA

Leave a Reply

- Advertisment -

MAFI SHAHARA

RA'AYOYIN JAMA'A

%d bloggers like this: