Thursday, March 23, 2023
HomeBatutuwaAdabiKungiyar CAN tace ba zata yarda APC ta tsaida Muslim da Muslim...

Kungiyar CAN tace ba zata yarda APC ta tsaida Muslim da Muslim takara ba a zaben 2023

Kungiyar CAN tace ba zata yarda APC ta tsaida Muslim da Muslim takara ba a zaben 2023

Daga Muryoyi

Kungiyar Kiristoci ta kasa CAN ta gargadi jam’iyyun siyasa a Najeriya da kada su kuskura su zabi Musulmi da Musulmi a matsayin yan takaran Shugaban kasa da mataimakinsa a zaben 2023.

A sanarwar da sakataren kungiyar na kasa, Joseph Bade Daramola, ya fitar a yau Juma’a CAN ta ce “Ba za ta taba yarda Tinubu ko Atiku su zabi Musulmi a matsayin mataimakansu ba”

- Advertisement -

Majiyar Muryoyi ta ruwaito kungiyar tace ko a yanzu da ake shinkafa da wake suna shan wahala ina ga mulki ya koma hannun Musulmai gaba daya.

Ta ce a yanzu ba 1993 bane lokacinda ake hada Musulmi da Musulmi amma CAN tace a yanzu kan mage ya waye hakan ba zata sabu ba.

Wannan dai na zuwa ne a lokacinda Hukumar zabe ta kasa INEC ta baiwa Tinubu da Atiku da su Kwankwaso wa’adin mako guda su mika sunayen abokan tafiyarsu

LABARAI MASU ALAKA

Leave a Reply

- Advertisment -

MAFI SHAHARA

RA'AYOYIN JAMA'A

%d bloggers like this: